Saturday, 8 August 2015

A FULANI TRADER WITH A DREAM OF BECOMING A PILOT

A young fulani boy that built a local remote control kite using solar panel and printed circuit board(PCB)

Friday, 7 August 2015

7 killed as gunmen attack hotel frequently used by UN peacekeepers in Mali

Suspected Islamic militia this morning attacked a hotel frequently used by UN peacekeepers in Sevare, Mali, killing 7 people. The gunmen stormed the hotel as early as 8am today, shooting sporadically and gaining access. 1 white man, 4 Malian soldiers & 2 terrorists died in the gun battle.
"It started before 8 a.m. (0800 GMT). I saw a body in front of the hotel. It was a white man but I don't know his nationality," said an eye witness told Reuters.
The hotel is believed to be lodging nationals from South Africa, France and Ukraine. A U.N. source, said that the attackers are still laying siege at the hotel.

Me ake ciki game da zaben shugaban PDP?

  • Sa'o'i 7 da suka wuce
Jam'iyyar PDP ta zamo babbar jam'iyyar adawa a Najeriya
A Najeriya, tun bayan mummunan kayen da jam'iyyar adawa ta PDP ta sha a zabukan da aka yi a watannin Maris da Aprilu inda mulkinta na shekaru 16 a jere ya kawo karshe, jam'iyyar take cikin rudani.
A watan Mayu ne, shugaban jam'iyyar, Alhaji Ahmadu Adamu Mu'azu ya yi murabus, al'amarin da yasa aka kafa shugabancin rikon kwarya na watanni uku karkashin jagorancin Alhaji Halliru Muhammad.
To yanzu watanni uku na sharadin rikon kwaryar na gab da cika, kuma batun maye gurbin shugaban jam'iyyar ne ya sake tasowa.
Sai dai wasu na ganin cewa dole ne kujerar shugaban jam'iyyar ta fito daga arewa maso gabashin kasar tunda tsohon shugaban, Ahmad Mu'azu murabus ya yi kafin wa'adinsa ya cika.
Kimanin mutane 20 ne dai suke takarar neman shugabancin jam'iyyar a halin yanzu.
Yanzu dai PDP ita ce babbar jam'iyyar adawa a Najeriya, bayan da jam'iyyar APC ta karbi mulki daga hannunta a zabukan da aka yi a watannin baya.

Nigeria za ta soma kera manyan makamai

  • Sa'a 1 da ta wuce
Dakarun Nigeria sun shafe shekaru shida suna yaki da Boko Haram
Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari ya ce kasar na shirin soma kera makamai domin dakarunta saboda a rage dogaro da makamai na kasashen waje.
"Mun umurci ma'aikatar tsaro ta fitar da tsari domin gina masana'antar samar da makamai a Nigeria," in ji Buhari.
Buhari ya kara da cewar zai yi wa kamfanin makamai na Kaduna watau DICON wanda aka kafa a shekarar 1964 garambawul domin soma aiki gadan-gadan.
Wata sanarwa da kakaki shugaban kasar, Garba Shehu ya fitar ta ce gwamnatin kasar za ta fitar da tsare-tsare domin ganin masana'antar ta koma ta zamani.
DICON a yanzu na kera kananan bindigogi ne da kuma wasu 'yan abubuwa na aikin farar- hula.
Dakarun Nigeria na bukatar makamai na zamani domin yaki da kungiyar Boko Haram wadda ta hallaka dubban mutane da kuma raba wasu fiye da miliyan daga muhallansu.